Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ayu 15:6-14 Littafi Mai Tsarki (HAU)

6. Ba na bukata in kā da kai,Kowace kalma da ka hurta ta kā da ka.

7. “Kana tsammani kai ne mutumin da aka haifa na farko?Sa'ad da Allah ya yi duwatsu kana nan?

8. Ko ka taɓa jin shirye-shiryen da Allah ya yi?Ko kai kaɗai kake da hikima a cikin mutane?

9. Ba wani abu da ka sani da mu ba mu sani ba.

10. Daga wurin mutanen da suka yi furfura muka koyi hikimarmu.Mun koyi hikimarmu daga mutane waɗanda aka haife suTun kafin a haifi mahaifinka.

11. “Allah yana ta'azantar da kai,Me ya sa har yanzu ka ƙi kulawa da shi?Mun yi magana a madadinsa a natse da lafazi mai daɗi.

12. Amma ka ta da hankalinka,Kana ta zazzare mana ido da fushi.

13. Fushi kake yi da Allah, kana ƙinsa.

14. Akwai mutumin da yake tsarkakakke sarai?Akwai mutumin da yake cikakke a wurin Allah?

Karanta cikakken babi Ayu 15