Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ayu 15:31-35 Littafi Mai Tsarki (HAU)

31. Idan wauta tasa ta kai shi ga dogara ga mugunta,To, mugunta ce kaɗai zai samu.

32. Kafin kwanakinsa su cika zai bushe,Zai bushe kamar reshe, ba zai ƙara yin ganye ba.

33. Zai ama kamar itacen inabiWanda 'ya'yansa suka kakkaɓe tun kafin su nuna,Kamar itacen zaitun wanda bai taɓa yin 'ya'ya ba.

34. Marasa tsoron Allah ba za su sami zuriya ba,Wuta za ta cinye gidajen da aka gina da dukiyar rashawa.

35. Waɗannan su ne irin mutanen da suke shirya tarzoma, su aikata mugunta.Kullum zuciyarsu cike take da ruɗarwa.”

Karanta cikakken babi Ayu 15