Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ayu 12:2-16 Littafi Mai Tsarki (HAU)

2. “Aha! Ashe, kai ne muryar jama'a,Idan ka mutu hikima ta mutu ke nan tare da kai.

3. Amma ni ma ina da hankali gwargwado, kamar yadda kake da shi,Ban ga yadda ka fi ni ba.Kowa ya san sukan abin da ka faɗa.

4. Har abokaina ma, suna ta yi mini dariya yanzu,Suna ta dariya ko da yake ni adali ne marar laifi,Amma akwai lokacin da Allah ya amsa addu'o'ina.

5. Ba ka shan wahalar kome, duk da haka ka maishe ni abin dariya.Ka bugi mutumin da yake gab da fāɗuwa.

6. Amma ɓarayi da marasa tsoronAllah suna zaune cikin salama,Ko da yake ƙarfinsu ne kaɗai allahnsu.

7. “Don haka tsuntsaye da dabbobi sun fi ka sani,Suna da abu mai yawa da za su koya maka.

8. Ka roƙi talikan da suke a duniya, da cikin teku, hikimar da suke da ita.

9. Dukansu sun sani ikon Ubangiji ne ya yi su.

10. Allah shi ne yake bi da rayukan talikansa.Numfashin dukan mutane kuwa a ikonsa yake.

11. Amma kamar yadda harsunanku suke jin daɗin ɗanɗanar abinci,Haka nan kuma kunnuwanku suke jin daɗin sauraren kalmomi.

12-13. “Tsofaffi suna da hikima,Amma Allah yana da hikima da iko.Tsofaffi suna da tsinkaya,Amma Allah yana da tsinkaya da ikon aikatawa.

14. Sa'ad da Allah ya rurrushe, wa zai iya sāke ginawa?Wa kuma zai iya fitar da mutumin da Allah ya sa a kurkuku?

15. Akan yi fari sa'ad da Allah ya hana ruwan sama,Rigyawa takan zo sa'ad da ya kwararo ruwa.

16. Allah mai iko ne a kullum kuwa cikin nasara yakeDa macuci, da wanda aka cutar, duk ƙarƙashin ikon Allah suke.

Karanta cikakken babi Ayu 12