Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

2 Tar 23:5-8 Littafi Mai Tsarki (HAU)

5. Sulusinsu kuma a fādar sarki, ɗayan sulusin kuwa a gangare, sauran jama'a duka kuwa a filayen Haikalin Ubangiji.

6. Amma kada kowa ya shiga Haikalin Ubangiji, sai dai firistoci da Lawiyawa masu hidima, su ne za su iya shiga, gama su tsarkaka ne. Amma dukan jama'a su kiyaye shari'a, kada su shiga Wuri Mai Tsarki na Ubangiji.

7. Lawiyawa za su kewaye sarkin, ko wanne da makamansa a hannu, duk wanda ya shiga ɗakin, sai a kashe shi. Su kuma kasance tare da sarki in zai shiga ko zai fita.”

8. Sai Lawiyawa da dukan Yahuza suka yi yadda Yehoyada, firist, ya umarta. Kowannensu ya kawo mutanensa waɗanda ba su aiki ran Asabar, da masu kama aiki ran Asabar, gama Yehoyada, firist, bai sallami ƙungiyoyin ba.

Karanta cikakken babi 2 Tar 23