Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

2 Sar 3:14-21 Littafi Mai Tsarki (HAU)

14. Elisha ya amsa ya ce, “Na rantse da Ubangiji Mai Runduna, wanda nake bautarsa, da ba domin ina ganin girman Yehoshafat Sarkin Yahuza ba, da ba zan kula da kai har ma in dube ka ba.

15. Amma yanzu ku kawo mini makaɗin garaya.”Da makaɗin garaya ya kaɗa, sai ikon Ubangiji ya sauko a kan Elisha.

16. Sai ya ce, “Ubangiji ya ce, ‘Ku haƙa kududdufai a kwarin nan.

17. Ko da yake ba ku ga iska, ko ruwan sama ba, duk da haka kwarin zai cika da ruwa domin ku sha, ku da dabbobinku.’

18. Wannan abu mai sauƙi ne a wurin Ubangiji, zai kuma ba da Mowabawa a hannunku.

19. Za ku ci kowane birni mai garu da kowane birni na musamman. Za ku sassare kowane kyakkyawan itace, ku kuma tattoshe maɓuɓɓugan ruwa. Za ku lalatar da gonaki masu kyau da duwatsu.”

20. Kashegari, da safe a lokacin miƙa hadaya, sai ga ruwa ya malalo daga wajen Edom har ƙasar ta cika da ruwa.

21. Da Mowabawa suka ji labari, sarakuna sun kawo musu yaƙi, sai dukan waɗanda suka isa ɗaukar makamai, daga ƙarami zuwa babba, aka kirawo su, suka ja dāga a kan iyaka.

Karanta cikakken babi 2 Sar 3