Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

2 Sar 2:20-25 Littafi Mai Tsarki (HAU)

20. Elisha kuwa ya ce, “Ku kawo mini gishiri a sabuwar ƙwarya.” Su kuwa suka kawo masa,

21. sai ya tafi maɓuɓɓugar ruwa yana barbaɗa gishirin, ya ce, “Haka Ubangiji ya ce, ‘Na warkar da wannan ruwa, ba zai ƙara sa a mutu ko a yi ɓari ba.’ ”

22. Ruwan kuwa ya gyaru bisa ga maganar Elisha, har wa yau.

23. Daga nan Elisha ya haura zuwa Betel. A hanya sai ga waɗansu samari sun fito daga cikin gari, suna yi masa eho, suna cewa, “Ka bar wurin nan, kai mai saiƙo.”

24. Elisha ya waiga, ya gan su, ya la'anta su da sunan Ubangiji. Sai waɗansu namomin jeji guda biyu suka fito daga cikin kurmi suka yayyage arba'in da biyu daga cikin samarin.

25. Daga nan Elisha ya tafi har Dutsen Karmel, sa'an nan ya koma Samariya.

Karanta cikakken babi 2 Sar 2