Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

2 Sam 22:18-33 Littafi Mai Tsarki (HAU)

18. Ya kuɓutar da ni daga waɗanda suke ƙina,Daga abokan gābana, waɗanda suka fi ƙarfina!

19. Sa'ad da nake cikin wahala sun auka mini,Amma Ubangiji ya kiyaye ni.

20. Ya taimake ni ya fisshe ni daga hatsari,Ya cece ni domin yana jin daɗina.

21. “Ubangiji ya sāka mini bisa ga adalcina,Ya sa mini albarka domin ba ni da laifin kome.

22. Gama na kiyaye dokar Ubangiji,Ban yi wa Allahna tayarwa ba.

23. Na kiyaye dukan dokokinsa,Ban yi rashin biyayya ga umarnansa ba.

24. Ya sani ni marar laifi ne,Na kiyaye kaina daga aikata mugunta.

25. Domin haka ya sāka mini bisa ga adalcina,Gama ya sani ba ni da laifi.

26. “Kai, ya Ubangiji, amintacce ne ga waɗanda suke da aminci,Nagari ne kuma ga waɗanda suke cikakku.

27. Mai Tsarki ne kai ga waɗanda suke tsarkaka,Amma kana gāba da waɗanda suke mugaye.

28. Kakan ceci masu tawali'u,Amma kakan ƙasƙantar da masu girmankai.

29. “Ya Ubangiji, kai ne haskena,Kana haskaka duhuna.

30. Ka ba ni ƙarfi don in auka wa abokan gābana,Da iko domin in murƙushe tsaronsu.

31. “Allahn nan cikakke ne ƙwarai,Maganarsa tabbatacciya ce!Kamar garkuwa yakeGa dukan masu neman kiyayewarsa.

32. Ubangiji shi kaɗai ne Allah,Allah ne kaɗai madogararmu.

33. Allahn nan shi ne mafaka, mai ƙarfi ne a gare ni,Ya sa hanyata ta zama lafiyayyiya.

Karanta cikakken babi 2 Sam 22