Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

2 Sam 22:16-26 Littafi Mai Tsarki (HAU)

16. An bayyana ƙarƙashin teku a fili,An tone tussan duniya,Lokacin da Ubangiji ya yi wa abokan gāba tsautawa,Ya yi musu ruri cikin fushi.

17. Daga Sama Ubangiji ya miƙo ya ɗauke ni,Ya tsamo ni daga zurfafan ruwaye.

18. Ya kuɓutar da ni daga waɗanda suke ƙina,Daga abokan gābana, waɗanda suka fi ƙarfina!

19. Sa'ad da nake cikin wahala sun auka mini,Amma Ubangiji ya kiyaye ni.

20. Ya taimake ni ya fisshe ni daga hatsari,Ya cece ni domin yana jin daɗina.

21. “Ubangiji ya sāka mini bisa ga adalcina,Ya sa mini albarka domin ba ni da laifin kome.

22. Gama na kiyaye dokar Ubangiji,Ban yi wa Allahna tayarwa ba.

23. Na kiyaye dukan dokokinsa,Ban yi rashin biyayya ga umarnansa ba.

24. Ya sani ni marar laifi ne,Na kiyaye kaina daga aikata mugunta.

25. Domin haka ya sāka mini bisa ga adalcina,Gama ya sani ba ni da laifi.

26. “Kai, ya Ubangiji, amintacce ne ga waɗanda suke da aminci,Nagari ne kuma ga waɗanda suke cikakku.

Karanta cikakken babi 2 Sam 22