Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

2 Sam 11:22-27 Littafi Mai Tsarki (HAU)

22. Manzon kuwa ya tafi ya faɗa wa Dawuda dukan abin da Yowab ya ce.

23. Ya ce, “Abokan gābanmu sun sami sa'a a kanmu. Sun fito su gabza da mu a karkara, amma muka kore su zuwa cikin ƙofar garin.

24. Sai maharba suka tsaya a kan garu daga ciki suka yi ta harbin barorinka. Waɗansu daga cikin barorin sarki sun mutu. Baranka Uriya Bahitte shi ma ya matu.”

25. Dawuda ya ce wa manzon, “Je ka ka faɗa wa Yowab kada wannan abu ya dame shi, ai, takobi ba ya tarar wanda zai kashe. Ku ƙara matsa wa garin lamba, ku faɗa masa har ku ragargaza shi. Ka ƙarfafa Yowab.”

26. Sa'ad da matar Uriya ta ji labarin mutuwar mijinta, ta yi makoki dominsa.

27. Da kwanakin makokin suka ƙare, sai Dawuda ya aika aka kawo ta gidansa, ta zama matarsa, ta haifa masa ɗa. Amma Ubangiji bai ji daɗin mugun abin nan da Dawuda ya yi ba.

Karanta cikakken babi 2 Sam 11