Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

2 Sam 1:16-22 Littafi Mai Tsarki (HAU)

16. Dawuda kuwa ya ce, “Alhakin jininka yana bisa kanka tun da yake da bakinka ka ce, ‘Ni ne na kashe wanda Ubangiji ya keɓe.’ ”

17. Sai Dawuda ya raira waƙar makoki domin Saul da Jonatan, ɗansa.

18. Ya umarta a koya wa mutanen Yahuza wannan waƙa. (An rubuta ta a littafin Yashar.)

19. “An kashe darajarki, ya Isra'ila, a kan tuddanki!Jarumawan sojojinmu sun fāɗi!

20. Kada a ba da labarin a Gat,Ko a titin Ashkelon.Kada ku sa matan Filistiyawa su yi murna,Kada ku sa 'yan matan arna su yi farin ciki.

21. “Kada ruwan sama ko raɓa su zubo kan tuddan Gilbowa.Da ma gonakinta su zama marasa ba da amfani.Gama a can ne aka zube garkuwoyin jarumawa a wulakance,Tsatsa ta rufe garkuwar Saul.

22. Bakan Jonatan mai kisa ne,Takobin Saul ba shi da jinƙai,Yana kashe masu iko, yana kuma kashe abokan gāba.

Karanta cikakken babi 2 Sam 1