Surori

  1. 1
  2. 2
  3. 3
  4. 4
  5. 5
  6. 6
  7. 7
  8. 8
  9. 9
  10. 10
  11. 11
  12. 12
  13. 13
  14. 14
  15. 15
  16. 16
  17. 17
  18. 18
  19. 19
  20. 20
  21. 21
  22. 22
  23. 23
  24. 24
  25. 25
  26. 26
  27. 27
  28. 28
  29. 29

Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

1 Tar 9 Littafi Mai Tsarki (HAU)

Waɗanda Suka Komo daga Babila

1. Haka kuwa aka lasafta Isra'ilawa bisa ga asalinsu. An rubuta su a littafin sarakunan Isra'ila.Sai aka kai mutanen Yahuza zaman talala a Babila saboda rashin amincinsu ga Ubangiji.

2. Waɗanda suka fara zama a biranen mallakarsu, su ne Isra'ilawa da firistoci, da Lawiyawa, da kuma ma'aikatan Haikali.

3. Waɗansu mutanen Yahuza, da na Biliyaminu, da na Ifraimu, da na Manassa suka zauna a Urushalima.

4-6. Iyalin Yahuza guda ɗari shida da tasa'in suka zauna a Urushalima, shugabansu kuwa shi ne Utai ɗan Ammihud, jīkan Omri daga wajen Feresa. Waɗansu kakanninsu kuwa su ne Imri da Bani. Zuriyar Shela ɗan Yahuza suna da shugaba mai suna Asaya. Zuriyar Zera ɗan Yahuza kuwa, shugabansu Yuwel.

7. Ga zuriyar Biliyaminu a Urushalima bi da bi, da Sallai ɗan Meshullam, da Hodawiya, da Hassenuwa,

8. da kuma Ibneya ɗan Yeroham, da Ila ɗan Uzzi, wato jīkan Mikri, da Meshullam ɗan Shefatiya, da Reyuwel, da Ibnija.

9. Tare da danginsu a zamaninsu, sun kai ɗari tara da hamsin da shida ne. Duk waɗannan shugabannin gidajen kakanninsu ne.

Firistocin da Suke a Urushalima

10. Daga cikin firistoci masu zama a Urushalima su ne Yedaiya, da Yehoyarib, da Yakin,

11. da Azariya ɗan Hilkiya, shi ne jami'in Haikalin Ubangiji, kakanninsa sun haɗu da Shallum ɗan Zadok, da Merayot, da Ahitub,

12. da Adaya ɗan Yeroham, kakanninsa sun haɗu da Fashur, da Malkiya, da Ma'asai ɗan Adiyel, kakanninsa sun haɗu da Yazera, da Meshullam, da Meshillemot, da Immer.

13. Firistacin da suke shugabannin gidajen kakanninsu, sun kai mutum dubu da ɗari bakwai da sittin (1,760). Ƙwararru ne cikin hidimar Haikalin Ubangiji.

14. Lawiyawa masu zama a Urushalima kuma, su ne Shemaiya ɗan Hasshub, wanda kakanninsa suka haɗu da Azrikam da Hashabiya daga 'ya'yan Merari, maza,

15. da kuma Bakbakkar, da Heresh, da Galal, da Mattaniya ɗan Mika wanda kakanninsa su ne Zikri da Asaf,

16. da kuma Obadiya ɗan Shemaiya, kakanninsa su ne Galal da Yedutun, da Berikiya ɗan Asa, wato jīkan Elkana, wanda ya zauna a garin Netofa.

17. Masu tsaron Haikalin, su ne Shallum, da Akkub, da Talmon, da Ahiman, da 'yan'uwansu. Shallum shi ne shugaba.

18. Har zuwa yau, iyalinsu suke tsaron ƙofar sarki a wajen gabas. A dā su ne suke tsaron sauran ƙofofin zangon Lawiyawa.

19. Shallum ɗan Kore, wato jīkan Ebiyasaf, tare da 'yan'uwansa na zuriyar Kora, suke lura da masu tsaron ƙofofin alfarwa kamar dai yadda kakanninsu suka lura da zangon Ubangiji.

20. A dā Finehas ɗan Ele'azara shi ne shugabansu, Ubangiji kuwa yana tare da shi.

21. Zakariya ɗan Shallum yake tsaron ƙofar alfarwa ta sujada.

22. Dukan waɗanda aka zaɓa domin su zama masu tsaron ƙofofi, su ɗari biyu ne da goma sha biyu. An lasafta su bisa ga asalinsu da garuruwansu. Dawuda da Sama'ila annabi, su ne suka sa su a matsayinsu na riƙon amana.

23. Saboda haka su da 'ya'yansu maza suke tsaron ƙofofin Ubangiji, wato alfarwa ta sujada.

24. Matsaran ƙofofi suka tsaya a kusurwoyi huɗu, wato gabas da yamma, kudu da arewa.

25. 'Yan'uwansu waɗanda suke a ƙauyuka kuwa, ya zamar musu wajibi su zo wurinsu kowane kwana bakwai, domin su karɓe su tsaron.

26. Su shugabanni huɗu na matsaran ƙofar Lawiyawa ne waɗanda suke da matsayi na riƙon amana, su ne masu lura da ɗakunan Haikalin Allah da dukiyarsa.

27. Sukan kwana suna tsaro kewaye da Haikalin Allah, gama hakkin yana kansu. Su ne sukan buɗe shi kowace safiya.

28. Waɗansunsu suna lura da kayayyakin aiki na cikin Haikali. Sukan ƙidaya su sa'ad da aka shigo da su, da sa'ad da aka fitar da su.

29. Aka sa waɗansu su zama masu lura da kayayyakin Haikalin, da kayayyakin aiki na cikin Wuri Mai Tsarki, da lallausan gari, da ruwan inabi, da mai, da turare, da kayan yaji.

30. Waɗansu 'ya'yan firistoci, maza, suke harhaɗa kayan yaji.

31. Mattitiya, ɗaya daga cikin Lawiyawa, ɗan farin Shallum na iyalin Kora, shi ne mai lura da toya waina.

32. Waɗansu 'yan'uwansu Kohatawa suke lura da gurasar ajiyewa. Sukan shirya ta kowace Asabar.

33. Waɗannan su ne mawaƙa, da shugabannin gidajen kakannin Lawiyawa, waɗanda suka zauna a ɗakunan Haikali, ba su yin wani aiki dabam, gama dare da rana suke yin aikinsu.

34. Waɗannan su ne manyan shugabannin gidajen kakannin Lawiyawa a zamaninsu, wato waɗanda suka zauna a Urushalima.

Kakannin Sarki Saul da Zuriyarsa

35. Yehiyel ne ya kafa Gibeyon ya zauna a ciki, sunan matarsa Ma'aka,

36. ɗan farinsa kuma shi ne Abdon. Sa'an nan ga Zur, da Kish, da Ba'al, da Ner, da Nadab,

37. da Gedor, da Ahiyo, da Zakariya, da Miklot,

38. mahaifin Shimeya. Zuriyarsu ne suka zauna a Urushalima daura da 'yan'uwansu.

39. Ner ya haifi Kish, Kish kuma ya haifi Saul, Saul ya haifi Jonatan, da Malkishuwa, da Yishwi, da Ish-boshet.

40. Jonatan ya haifi Mefiboshet, Mefiboshet ya haifi Mika.

41. 'Ya'yan Mika, maza, su ne Fiton, da Melek, da Tareya, da Ahaz.

42. Ahaz ya haifi Yehowadda, Yehowadda ya haifi Allemet, da Azmawet, da Zimri. Zimri ya haifi Moza,

43. Moza ya haifi Bineya, da Refaya, da Eleyasa, da Azel.

44. Azel yana da 'ya'ya maza guda shida, su ne Azrikam, da Bokeru, da Isma'ilu, da Sheyariya, da Obadiya, da Hanan.