Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

1 Tar 29:25-30 Littafi Mai Tsarki (HAU)

25. Ubangiji kuwa ya ɗaukaka Sulemanu ƙwarai da gaske a gaban dukan Isra'ilawa, ya ɗaukaka sarautarsa fiye da ta waɗanda suka riga shi sarauta a Isra'ila.

26. Dawuda ɗan Yesse ya yi mulki bisa dukan Isra'ila,

27. har shekara arba'in. Ya yi mulki a Hebron shekara bakwai sa'an nan ya yi mulki shekara talatin da uku a Urushalima.

28. Sa'an nan ya rasu da kyakkyawan tsufa, cike da shekaru, da arziki, da daraja. Ɗansa Sulemanu kuma ya gāji sarautarsa.

29. An fa rubuta ayyukan sarki Dawuda daga farko har ƙarshe a tarihin Sama'ila, annabi, da na annabi Natan, da na annabi Gad.

30. An rubuta labarin mulkinsa, da ikonsa, da al'amuran da suka same shi, da Isra'ilawa, da dukan mulkokin ƙasashe na kewaye.

Karanta cikakken babi 1 Tar 29