Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

1 Tar 26:2-12 Littafi Mai Tsarki (HAU)

2. Shallum kuwa yana da 'ya'ya maza, su ne Zakariya, da Yediyayel, da Zabadiya, da Yatniyel,

3. da Elam, da Yehohanan, da Eliyehoyenai, su bakwai ke nan.

4. Obed-edom kuma Allah ya ba shi 'ya'ya maza, su ne Shemaiya, da Yehozabad, da Yowa, da Sakar, da Netanel,

5. da Ammiyel, da Issaka, da Fauletai, da su Allah ya sa masa albarka.

6. Ɗan farin Obed-edom, wato Shemaiya ya haifi 'ya'ya maza waɗanda suka yi shugabanci a gidan kakansu, gama su jarumawa ne.

7. 'Ya'yan Shemaiya, su ne Otni, da Refayel, da Obida, da Elzabad, waɗanda 'yan'uwansu, Elihu, da Semakiya jarumawa ne.

8. Waɗannan duka iyalin Obed-edom ne. Su da 'ya'yansu maza da 'yan'uwansu suna da ƙarfi da gwaninta na yin aiki. Su sittin da biyu ne daga wajen Obed-edom.

9. Shallum yana da 'ya'ya maza da 'yan'uwa, su goma sha takwas jarumawa.

10. Hosa kuma na wajen 'ya'yan Merari, maza, yana da 'ya'ya maza, Shimri shi ne babba, ko da yake ba shi ne ɗan fari ba, duk da haka mahaifinsa ya maishe shi babba.

11. Hilkiya shi ne na biyu, da Tebaliya na uku, da Zakariya na huɗu. Dukan 'ya'yan Hosa, maza, da 'yan'uwansa, su goma sha uku ne.

12. Aka rarraba masu tsaron Haikali ƙungiya ƙungiya, bisa ga iyali, aka raba musu ayyuka a Haikali kamar dai sauran Lawiyawa.

Karanta cikakken babi 1 Tar 26