Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

1 Tar 23:22-25 Littafi Mai Tsarki (HAU)

22. Ele'azara kuwa ya rasu ba shi da 'ya'ya maza, sai 'yan mata kaɗai, sai 'yan'uwansu, 'ya'yan Kish, maza, suka aure su.

23. 'Ya'yan Mushi, maza, su uku ne, wato Mali, da Eder, da Yerimot.

24. Waɗannan su ne 'ya'yan Lawi, maza, bisa ga gidajen kakanninsu, wato su ne shugabannin da aka rubuta sunayensu ɗaya ɗaya daga mai shekara ashirin da haihuwa zuwa sama. Su ne za su yi hidima a cikin Haikalin Ubangiji.

25. Gama Dawuda ya ce, “Ubangiji Allah na Isra'ila ya hutar da jama'arsa, yana kuwa zama a Urushalima har abada.

Karanta cikakken babi 1 Tar 23