Arauna ya ce wa Dawuda, “Ka karɓa, na ba ka, sai ka yi abin da kake so da ita, ranka ya daɗe. Zan kuma ba da bijimai domin hadayu na ƙonawa, in ba da keken sussuka domin itacen wuta, in kuma ba da alkama don hadaya ta gari. Zan ba ka waɗannan duka.”