Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

1 Tar 11:4-11 Littafi Mai Tsarki (HAU)

4. Sarki Dawuda kuwa, tare da dukan Isra'ilawa, suka tafi Urushalima, wato Yebus inda Yebusiyawa suke zaune.

5. Sai mazaunan Yebus, suka ce wa Dawuda, “Ba za ka shiga nan ba.” Duk da haka Dawuda ya ci Sihiyona, gari mai kagara, wato birnin Dawuda ke nan.

6. Sai Dawuda ya ce, “Duk wanda ya ci Yebusiyawa da fari shi ne zai zama babban shugaban sojoji.” Yowab ɗan Zeruya ne ya fara tafiya, domin wannan aka maishe shi shugaba.

7. Sa'an nan Dawuda ya zauna a kagara, don haka aka kira birnin, birnin Dawuda.

8. Sai ya rutsa birnin da gini tun daga Millo. Yowab kuma ya gyaggyara sauran birnin.

9. Dawuda ya yi ta ƙasaita gaba gaba saboda Ubangiji Mai Runduna yana tare da shi.

10. Waɗannan su ne shugabanni, wato manyan jarumawan Dawuda waɗanda suka goyi bayansa sosai a mulkinsa, tare da dukan Isra'ilawa waɗanda suka naɗa shi sarki bisa ga maganar Ubangiji a kan Isra'ilawa.

11. Wannan shi ne labarin manyan jarumawan Dawuda. Yashobeyam ɗan Bahakmone shi ne shugaban jarumawa talatin. Ya karkashe mutum ɗari uku da māshinsa baki ɗaya.

Karanta cikakken babi 1 Tar 11