Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

1 Sar 3:24-28 Littafi Mai Tsarki (HAU)

24. Sai ya umarta a kawo takobi. Da aka kawo takobin,

25. sai ya ce, “A raba ɗan nan mai rai kashi biyu, kowacce ta ɗauki rabi.”

26. Saboda zuciyar mahaifiyar ta ainihi ta cika da juyayin ɗanta, ta ce wa sarki, “Ranka ya daɗe kada a kashe yaron! A ba ta!”Amma ɗayar ta ce, “Kada a ba kowa daga cikinmu, a ci gaba a raba shi.”

27. Sa'an nan Sulemanu ya ce, “Kada ku kashe yaron! Ku miƙa wa ta farin, ita ce mahaifiyarsa ta ainihi.”

28. Sa'ad da dukan mutanen Isra'ila suka ji shari'ar da sarki ya yanke, sai suka girmama shi ƙwarai, gama sun gane Allah ya ba shi hikimar daidaita husuma sosai.

Karanta cikakken babi 1 Sar 3