Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

1 Sar 20:17-21 Littafi Mai Tsarki (HAU)

17. Samarin ne suka fara fita. Sai Ben-hadad ya aiki mutane, suka faɗa masa cewa, “Mutane suna zuwa daga Samariya.”

18. Sai ya ce, “Ku kama su da rai, ko sun zo da nufin salama ko da na yaƙi.”

19. Waɗannan kuwa suka fita daga birnin, wato sojoji matasa, rundunar Isra'ilawa kuma tana biye da su,

20. kowa ya kashe abokin gābansa. Suriyawa kuwa suka gudu, Isra'ilawa kuma suka runtume su. Amma Ben-hadad, Sarkin Suriya, ya tsere kan doki tare da mahayan dawakai.

21. Sarkin Isra'ila ya fita, ya ƙwace dawakai da karusai, ya kashe Suriyawa da yawa.

Karanta cikakken babi 1 Sar 20