Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

1 Sar 2:4-19 Littafi Mai Tsarki (HAU)

4. domin Ubangiji ya cika maganar da ya faɗa mini cewa, ‘Idan 'ya'yanka suna lura da hanyarsu, sun yi tafiya a gabana da gaskiya da zuciya ɗaya, da dukan ransu, ba za ka rasa mutum wanda zai hau gadon sarautar Isra'ila ba.’

5. “Ka kuma san abin da Yowab ɗan Zeruya ya yi mini, yadda ya kashe shugabannin sojoji na Isra'ila su biyu, wato Abner ɗan Ner, da Amasa ɗan Yeter. Ya zubar da jinin yaƙi a lokacin salama. Ya sa jinin yaƙi a kan ɗamararsa wadda take gindinsa, da kuma kan takalmansa da yake ƙafafunsa.

6. Ka san abin da za ka yi, kada ka bar shi ya mutu ta hanyar lafiya.

7. “Amma ka nuna alheri ga 'ya'yan Barzillai daga Gileyad, ka lura da su da kyau, gama sun nuna mini alheri sa'ad da nake gudu daga ɗan'uwanka, Absalom.

8. “Ga kuma Shimai ɗan Gera, daga garin Bahurim ta Biliyaminu. Shi ne ya yi mini mugun zagi sa'ad da na tafi Mahanayim, amma sa'ad da ya zo taryata a Urdun, sai na rantse masa da Ubangiji, na ce ba zan kashe shi ba.

9. Don haka dole ka hukunta shim, ka dai san abin da za ka yi da shi, lalle ne kuma za ka ga an kashe shi.”

10. Sa'an nan Dawuda ya rasu, aka binne shi a birnin Urushalima.

11. Ya yi shekara arba'in yana sarautar Isra'ila. Ya yi mulki shekara bakwai a Hebron, sa'an nan ya yi shekara talatin da uku yana mulki a Urushalima.

12. Sulemanu kuwa ya hau gadon sarautar ubansa, Dawuda. Mulkinsa kuma ya kahu sosai.

13. Sa'an nan Adonija ɗan Haggit ya tafi wurin Bat-sheba, tsohuwar Sulemanu. Ta ce masa, “Ka zo lafiya?”Ya ce, “Lafiya lau.”

14. Sa'an nan ya ce, “Ina da wani abin da zan faɗa miki.”Ta ce, “To, sai ka faɗa.”

15. Ya amsa ya ce, “Kin sani dai sarauta tawa ce. Ni ne kuwa mutanen Isra'ila duka suka sa zuciya zan ci sarautar, amma al'amarin ya sāke, sai sarautar ta zama ta ƙanena , gama tasa ce bisa ga nufin Allah.

16. Yanzu dai ina da roƙo guda zuwa gare ki, kada ki hana mini.”

17. Ta ce masa, “To, sai ka faɗa.”Sai ya ce, “In kin yarda ki yi magana da sarki Sulemanu, gama ba zai ƙi jinki ba, ki ce ya ba ni yarinyar nan, Abishag, daga Shunem, ta zama matata.”

18. Bat-sheba kuwa ta ce, “Da kyau, zan yi wa sarki magana dominka.”

19. Sa'an nan Bat-sheba ta tafi wurin sarki Sulemanu don ta yi magana da shi a kan Adonija. Sarki ya tashi domin ya tarye ta. Ya rusuna mata, sa'an nan ya zauna a kujerar sarautarsa. Ya sa aka kawo mata kujera, ta kuwa zauna a wajen damansa.

Karanta cikakken babi 1 Sar 2