Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

1 Sar 14:22-26 Littafi Mai Tsarki (HAU)

22. Mutanen Yahuza suka yi wa Ubangiji zunubi. Suka tsokane shi ya yi fushi saboda zunuban da suka aikata fiye da abin da kakanninsu suka yi.

23. Gama su ma sun gina wa kansu wuraren tsafi a tuddai, da ginshiƙai, da gumaka a tuddai, da cikin duhuwar itatuwa.

24. Fiye da haka kuma akwai mata da maza da suke aikin karuwanci a wuraren da suke tsafin a wurin al'ummai. Mutanen Yahuza sun yi dukan abubuwan ƙazanta na al'ummai waɗanda Ubangiji ya kora sa'ad da Isra'ilawa suke gab da shigar ƙasar.

25. A cikin shekara ta biyar ta sarautar sarki Rehobowam, sai Shishak Sarkin Masar ya kai wa Urushalima yaƙi.

26. Ya kwashe dukiyar Haikalin Ubangiji, da dukiyar gidan sarki duka. Ya kuma kwashe garkuwoyin zinariya waɗanda Sulemanu ya yi.

Karanta cikakken babi 1 Sar 14