Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

1 Sam 9:24-27 Littafi Mai Tsarki (HAU)

24. Sai mai dahuwa ya kawo cinya da gadon baya ya ajiye a gaban Saul. Sa'an nan Sama'ila ya ce, “Sai ka ci naman da aka ajiye a gabanka, gama dominka aka ajiye shi don ka ci a wannan lokaci tare da waɗanda na gayyata.”A wannan rana kuwa Saul ya ci tare da Sama'ila.

25. Sa'ad da suka gangaro daga wurin yin sujadar zuwa cikin gari, sai aka shirya wa Saul gado a kan bene.

26. Ya kwanta, ya yi barci.Da asuba, Sama'ila ya kira Saul ya ce, “Tashi, in sallame ka.” Saul kuwa ya tashi, shi da Sama'ila suka fita waje zuwa kan titi.

27. Sa'ad da suka kai bayan gari, sai Sama'ila ya ce wa Saul, “Ka sa baranka ya yi gaba, kai ka tsaya nan tukuna domin in faɗa maka abin da Allah ya ce.”

Karanta cikakken babi 1 Sam 9