Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Yah 9:22-27 Littafi Mai Tsarki (HAU)

22. Iyayensa sun faɗi haka ne don tsoron Yahudawa, don dā ma Yahudawa sun ƙulla, cewa kowa ya amsa, cewa shi ne Almasihu, za a fisshe shi daga jama'a.

23. Shi ya sa iyayensa suka ce, “Ai, ba yaro ba ne, ku tambaye shi.”

24. Sai suka sāke kiran mutumin nan da yake makaho a dā, suka ce masa, “Ka tsoraci Allah dai! Mu kam, mun san mutumin nan mai zunubi ne.”

25. Sai ya amsa ya ce, “Ko mai zunubi ne, ni ban sani ba. Abu ɗaya kam, na sani, dā ni makaho ne, yanzu kuwa ina gani.”

26. Sai suka ce masa, “Shin, me ya yi maka? Ta yaya ya buɗe maka ido?”

27. Ya amsa musu ya ce, “Na riga na faɗa muku, ba ku ji ba. Don me kuke so ku sāke ji? Ko ku ma kuna so ku zama almajiransa ne?”

Karanta cikakken babi Yah 9