Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Yah 9:1-5 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Yesu na wucewa sai ya ga wani mutum da aka haifa makaho.

2. Sai almajiransa suka tambaye shi suka ce, “Ya Shugaba, wa ya yi zunubi da aka haifi mutumin nan makaho, shi, ko iyayensa?”

3. Yesu ya amsa ya ce, “Ba domin mutumin nan ko iyayensa sun yi zunubi ba, sai domin a nuna aikin Allah ne a kansa.

4. Lalle ne mu yi aikin wanda ya aiko ni tun da sauran rana. Ai, dare zai yi sa'ad da ba mai iya aiki.

5. Muddin ina duniya ni ne hasken duniya.”

Karanta cikakken babi Yah 9