Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Yah 8:1-7 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Yesu kuwa ya hau Dutsen Zaitun.

2. Da sassafe kuma ya sāke shiga Haikali. Duk mutane suka zo wurinsa, ya kuwa zauna yana koya musu.

3. Sai malaman Attaura da Farisiyawa suka kawo wata mace da aka kama da zina. Da suka tsai da ita a tsaka,

4. suka ce masa, “Malam, matan nan an kama ta ne, suna cikin yin zina.

5. To, a Attaura Musa ya umarce mu mu kashe irin waɗannan da jifa, kai kuwa me ka ce?”

6. Sun faɗi haka ne don su gwada shi, ko sa sami hanyar kai ƙararsa. Amma Yesu ya sunkuya, ya yi ta rubutu a ƙasa da yatsa.

7. Da suka dinga tambayarsa sai ya ɗaga, ya ce musu, “To, marar zunubi a cikinku ya fara jifanta da dutse.”

Karanta cikakken babi Yah 8