Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Yah 6:44-47 Littafi Mai Tsarki (HAU)

44. Ba mai iya zuwa wurina, sai dai in Uba wanda ya aiko ni ne ya jawo shi, ni kuwa zan tashe shi a ranar ƙarshe.

45. A rubuce yake cikin littattafan annabawa cewa, ‘Dukkansu Allah ne zai koya musu.’ To, duk wanda ya ji, ya kuma koya wurin Uba, zai zo gare ni.

46. Ba wai don wani ya taɓa ganin Uban, sai shi wanda yake daga wurin Allah, shi ne ya ga Uban.

47. Lalle hakika ina gaya muku, wanda ya ba da gaskiya, yana da rai madawwami.

Karanta cikakken babi Yah 6