Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Yah 6:40-52 Littafi Mai Tsarki (HAU)

40. Gama nufin Ubana, shi ne duk wanda yake duban Ɗan, yake kuma gaskatawa da shi, yă sami rai madawwani, ni kuma zan tashe shi a ranar ƙarshe.”

41. Sai fa Yahudawa suka yi masa gunaguni, domin ya ce, “Ni ne Gurasan da ya sauko daga Sama.”

42. Suka ce, “Ashe, wannan ba Yesu ba ne, ɗan Yusufu, wanda uwa tasa da ubansa duk mun san su? To, yaya yanzu zai ce, ‘Na sauko ne daga sama’?”

43. Yesu ya amsa musu ya ce, “Kada ku yi gunaguni a junanku.

44. Ba mai iya zuwa wurina, sai dai in Uba wanda ya aiko ni ne ya jawo shi, ni kuwa zan tashe shi a ranar ƙarshe.

45. A rubuce yake cikin littattafan annabawa cewa, ‘Dukkansu Allah ne zai koya musu.’ To, duk wanda ya ji, ya kuma koya wurin Uba, zai zo gare ni.

46. Ba wai don wani ya taɓa ganin Uban, sai shi wanda yake daga wurin Allah, shi ne ya ga Uban.

47. Lalle hakika ina gaya muku, wanda ya ba da gaskiya, yana da rai madawwami.

48. Ni ne Gurasa mai ba da rai.

49. Kakannin kakanninku sun ci manna a jeji, amma kuwa sun mutu.

50. Ga Gurasa mai saukowa daga Sama, domin kowa yă ci, kada ya mutu.

51. Ni ne Gurasan rai da ya sauko daga Sama. Kowa ya ci Gurasan nan, zai rayu har abada. Har ma gurasar da zan bayar naman jikina ne, domin duniya ta rayu.”

52. Sai Yahudawa suka ta da husuma a junansu, suna cewa, “Yaya mutumin nan zai iya ba mu naman jikinsa mu ci?”

Karanta cikakken babi Yah 6