Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Yah 21:6-10 Littafi Mai Tsarki (HAU)

6. Ya ce musu, “Ku jefa taru dama da jirgin za ku samu.” Suka jefa, har suka kāsa jawo shi don yawan kifin.

7. Sai almajirin nan da Yesu yake ƙauna ya ce wa Bitrus, “Ubangiji ne dai!” Da Bitrus ya ji, ashe, Ubangiji ne ya yi ɗamara da taguwarsa, don a tuɓe yake, ya fāɗa tekun.

8. Sauran almajirai kuwa suka zo a cikin ƙaramin jirgi, janye da tarun cike da kifi, don ba su da nisa daga gaci, kamar misalin kamu ɗari biyu ne.

9. Da fitowarsu gaci sai suka ga garwashi a wurin, da kifi kai, da kuma gurasa.

10. Yesu ya ce musu, “Ku kawo waɗansu kifi a na waɗanda kuka kama yanzu.”

Karanta cikakken babi Yah 21