Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Yah 11:23-26 Littafi Mai Tsarki (HAU)

23. Yesu ya ce mata, “Ɗan'uwanki zai tashi.”

24. Marta ta ce masa, “Na sani zai tashi a tashin matattu a ranar ƙarshe.”

25. Yesu ya ce mata, “Ai, ni ne tashin matattu, ni ne kuma rai. Wanda ya gaskata da ni, ko ya mutu zai rayu.

26. Wanda kuwa yake raye, yake kuma gaskatawa da ni, ba zai mutu ba har abada. Kin gaskata wannan?”

Karanta cikakken babi Yah 11