Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Yah 11:11-17 Littafi Mai Tsarki (HAU)

11. Ya faɗi haka, sa'an nan ya ƙara ce musu, “Amininmu Li'azaru ya yi barci, amma za ni in tashe shi.”

12. Sai almajiran suka ce masa, “Ya Ubangiji, in dai barci ne ya ɗauke shi, ai, zai warke.”

13. Alhali kuwa, Yesu zancen mutuwar Li'azaru yake, amma su sun ɗauka yana nufin barcin hutawa ne.

14. Sai Yesu ya gaya musu a fili, ya ce, “Li'azaru dai ya mutu.

15. Ina kuwa farin ciki da ba na nan, saboda ku domin ku ba da gaskiya. Amma mu dai je wurinsa.”

16. Sai Toma, wanda ake kira Ɗan Tagwai, ya ce wa 'yan'uwansa almajirai, “Mu ma mu tafi, mu mutu tare da shi.”

17. Da Yesu ya isa, ya tarar Li'azaru, har ya kwana huɗu a kabari.

Karanta cikakken babi Yah 11