Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Yah 1:4-7 Littafi Mai Tsarki (HAU)

4. Shi ne tushen rai, wannan rai kuwa shi ne hasken mutane.

5. Haske na haskakawa cikin duhu, duhun kuwa bai rinjaye shi ba.

6. Akwai wani mutum da Allah ya aiko, mai suna Yahaya.

7. Shi fa ya zo shaida ne, domin ya shaidi hasken, kowa yă ba da gaskiya ta hanyarsa.

Karanta cikakken babi Yah 1