Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Rom 8:14-17 Littafi Mai Tsarki (HAU)

14. Duk waɗanda Ruhun Allah yake bishe su, su ne 'ya'yan Allah.

15. Ai, ruhun da kuka samu ba na bauta ba ne, har da za ku koma zaman tsoro. A'a, na zaman 'ya'ya ne, har muna kira, “Ya Abba! Uba!”

16. Ruhu da Kansa ma, tare da namu ruhu suna yin shaida, cewa mu 'ya'yan Allah ne.

17. In kuwa 'ya'ya muke, ashe, magāda ne kuma, magādan Allah, abokan gādo kuma da Almasihu, in dai har muna shan wuya tare da shi, a kuwa ɗaukaka mu tare da shi.

Karanta cikakken babi Rom 8