Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Rom 5:5-16 Littafi Mai Tsarki (HAU)

5. ita sa zuciyar nan kuwa ba ta sāce iska faufau, domin Allah ya kwarara ƙaunarsa a zukatanmu, ta wurin Ruhu Mai Tsarki da aka ba mu.

6. Tun muna raunana tukuna, Almasihu ya mutu a daidaitaccen lokaci, domin marasa bin Allah.

7. Da ƙyar za a sami wanda zai ba da ransa, saboda mutum mai adalci, ko da yake watakila saboda mutum mai nagarta wani ma sai yă yi kasai da ransa.

8. Amma kuwa Allah yana tabbatar mana da ƙaunar da yake yi mana, wato tun muna masu zunubi, Almasihu ya mutu dominmu.

9. To, tun da yake a yanzu an kuɓutar da mu ta wurin jininsa, ashe kuwa, ta wurinsa za mu fi samun kārewa daga fushin Allah ke nan.

10. In kuwa tun muna maƙiyan Allah aka sulhunta mu da shi ta mutuwar Ɗansa, to, da yake an sulhunta mu, ashe kuwa, za a fi kāre mu ta wurin rayuwarsa ke nan.

11. Banda haka ma, har muna fariya da Allah ta wurin Ubangijinmu Yesu Almasihu, wanda ta wurinsa ne muka sami sulhun nan a yanzu.

12. To, kamar yadda zunubi ya shigo duniya ta dalilin mutum ɗaya, zunubi kuwa shi ya jawo mutuwa, ta haka mutuwa ta zama gādo ga kowa, don kowa ya yi zunubi.

13. Lalle fa zunubi yana nan a duniya tun ba a ba da Shari'a ba, sai dai inda ba shari'a, ba a lasafta zunubi.

14. Duk da haka kuwa mutuwa ta mallaka tun daga Adamu har ya zuwa Musa, har ma a kan waɗanda ba su yi zunubi irin na keta umarnin da adamu ya yi ba, wanda yake shi ne kwatancin mai zuwan nan.

15. Amma fa baiwar nan dabam take ƙwarai da laifin nan. Ai, in laifin mutum ɗayan nan ya jawo wa masu ɗumbun yawa mutuwa, ashe ma, alherin Allah, da kuma baiwar nan, albarkacin alherin Mutum ɗaya, Yesu Almasihu, sai su yalwata ga masu ɗumbun yawa fin haka ƙwarai.

16. Baiwar nan kuwa dabam take ƙwarai da hakkokin zunubin mutum ɗayan nan. Don kuwa hukuncin da aka yi a kan laifin mutum ɗayan nan, shi ya jawo hukuncin hallaka. Amma baiwar nan da aka yi a sanadin laifofi da yawa, ita take sa kuɓuta ga Allah.

Karanta cikakken babi Rom 5