Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Rom 2:10-15 Littafi Mai Tsarki (HAU)

10. Amma Allah zai ba da daraja, da ɗaukaka, da salama ga dukan waɗanda suke aikata nagarta, da fari ga Yahudawa, sa'an nan ga al'ummai.

11. Domin kuwa, Allah ba ya nuna tara.

12. Ɗaukacin waɗanda suka yi zunubi a rashin sanin Shari'a, za su hallaka ne ba tare da Shari'a ba. Ɗaukacin waɗanda suka yi zunubi a ƙarƙashin Shari'a kuwa, za a hukunta su ta hanyar Shari'a.

13. Don ba ta jin shari'ar kawai mutum yake samun kuɓuta ga Allah ba, sai dai masu aikata ta, su ne za su kuɓuta.

14. In al'ummai, su da ba su da Shari'a, jikinsu ya ba su suka bi umarnin Shari'a, ko da yake ba su da Shari'ar, ashe kuwa, suna da shari'a ke nan.

15. Ayyukansu sun nuna, cewa abin da Shari'a ta umarta a rubuce yake a cikin zukatansu, lamirinsu kuwa yana shaidawa, tunaninsu kuwa yana zarginsu, ko kuma yana kāre su.

Karanta cikakken babi Rom 2