Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mat 4:18-21 Littafi Mai Tsarki (HAU)

18. Yana tafiya a bakin Tekun Galili ke nan, sai ya ga waɗansu 'yan'uwa biyu, Saminu da ake kira Bitrus, da ɗan'uwansa Andarawas, suna jefa taru a teku, don su masunta ne.

19. Sai ya ce musu, “Ku bi ni, zan mai da ku masuntan mutane.”

20. Nan da nan, sai suka watsar da tarunansu, suka bi shi.

21. Da ya ci gaba sai ya ga waɗansu mutum biyu, su kuma 'yan'uwa ne, Yakubu ɗan Zabadi, da ɗan'uwansa Yahaya, suna cikin jirgi tare da ubansu Zabadi, suna gyaran tarunansu. Sai ya kira su.

Karanta cikakken babi Mat 4