Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mat 27:48-52 Littafi Mai Tsarki (HAU)

48. Sai nan da nan ɗaya daga cikinsu ya yiwo gudu, ya ɗauko soso ya jiƙa shi da ruwan tsami, ya soka a sanda, ya miƙa masa yă sha.

49. Amma sauran suka ce, “Ku bari mu gani ko Iliya zai zo ya ceci shi.”

50. Sai Yesu ya sāke ɗaga murya da ƙarfi, sa'an nan ya săki ransa.

51. Sai labulen da yake cikin Haikalin ya tsage gida biyu, daga sama har ƙasa. Ƙasa ta yi girgiza, duwatsu kuma suka tsattsage.

52. Aka bubbuɗe kaburbura, tsarkaka da yawa da suke barci kuma suka tashi.

Karanta cikakken babi Mat 27