Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mat 24:39-45 Littafi Mai Tsarki (HAU)

39. ba su farga ba har Ruwan Tsufana ya zo ya share su. Haka komowar Ɗan Mutum za ta zama.

40. A sa'an nan za a ga mutum biyu a gona, a ɗau ɗaya, a bar ɗaya.

41. Za a ga mata biyu suna niƙa, a ɗau ɗaya, a bar ɗaya.

42. To, ku zauna a faɗake fa, don ba ku san ranar da Ubangijinku zai dawo ba.

43. Amma dai ku sani, da maigida zai san ko a wane lokaci ne da dare ɓarawo zai zo, da ya zauna a faɗake ya hana a shigar masa gida.

44. Don haka ku ma sai ku zauna a kan shiri, domin a lokacin da ba ku zata ba, Ɗan Mutum zai zo.”

45. “Wane ne amintaccen bawan nan mai hikima, da ubangidansa ya ba shi riƙon gidansa, yă riƙa ba su abincinsu a kan kari?

Karanta cikakken babi Mat 24