5. Duk ayyukansu suna yi ne don idon mutane, suna yin layunsu fantam-fantam, lafin rigunansu kuma har gwiwa.
6. Suna son mazaunan alfarma a wurin biki, da mafifitan mazaunai a majami'u,
7. a gaishe su a kasuwa, a kuma riƙa ce da su ‘Malam’.
8. Amma ku kam, kada a ce muku ‘Malam’, domin Malaminku ɗaya ne, ku duka kuwa 'yan'uwa ne.
9. Kada ku kira kowa ‘Uba’ a duniya, domin Uba ɗaya ne yake gare ku, wanda yake cikin Sama.
10. Kada kuma a kira ku ‘Shugabanni’, domin Shugaba ɗaya gare ku, wato, Almasihu.
11. Amma wanda yake babba a cikinku shi zai zama baranku.