Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mat 22:1-8 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Yesu ya sāke yi musu magana da misalai ya ce,

2. “Za a kwatanta Mulkin Sama da wani sarki, wanda ya yi wa ɗansa biki.

3. Sai ya aiki bayinsa su kirawo waɗanda aka gayyata bikin, amma waɗanda aka gayyatar suka ƙi zuwa.

4. Har wa yau ya sāke aiken waɗansu bayi, ya ce, ‘Ku gaya wa waɗanda aka gayyata, “Ga shi, na shisshirya abinci, an yanka shanuna da kiwatattun maruƙana, duk an shirya kome, ku zo bikin mana!” ’

5. Amma suka ƙi kula, suka tafi abinsu, wani ya tafi gona tasa, wani kuma cinikinsa.

6. Sauran kuwa suka kame bayinsa, suka wulaƙanta su, suka kashe su.

7. Sarki ya yi fushi, ya tura sojansa, suka hallaka masu kisankan nan, suka ƙone garinsu ƙurmus.

8. Sa'an nan ya ce wa bayinsa, ‘Bikin fa ya shiryu sosai, amma waɗanda aka gayyata ba su cancanta ba.

Karanta cikakken babi Mat 22