Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mat 2:1-8 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Sa'ad da aka haifi Yesu a Baitalami ta ƙasar Yahudiya, a zamanin sarki Hirudus, sai ga waɗansu masana taurari daga gabas suka zo Urushalima, suna cewa,

2. “Ina wanda aka haifa Sarkin Yahudawa? Domin mun ga tauraronsa a gabas, mun kuma zo mu yi masa sujada.”

3. Da sarki Hirudus ya ji haka, sai ya damu ƙwarai, haka kuma dukan mutanen Urushalima.

4. Sai ya tara dukan manyan firistoci da malaman Attaura na jama'a, ya tambaye su inda za a haifi Almasihu.

5. Sai suka ce masa, “A Baitalami ne, ta ƙasar Yahudiya, domin haka annabin ya rubuta cewa,

6. ‘Ke ma Baitalami, ta kasar Yahuza,Ko kusa ba ke ce mafi ƙanƙanta a cikin manyan garuruwan Yahuza ba,Domin daga cikinki za a haifi wani mai mulki,Wanda zai zama makiyayin jama'ata, Isra'ila.’ ”

7. Sai Hirudus ya kira masanan nan a asirce, ya tabbata daga bakinsu ainihin lokacin da tauraron nan ya bayyana.

8. Sa'an nan ya aike su Baitalami, ya ce, “Ku je ku binciko mini ɗan yaron nan sosai. In kun same shi, ku kawo mini labari, don ni ma in je in yi masa sujada.”

Karanta cikakken babi Mat 2