Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mat 19:1-4 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. To, da Yesu ya gama duk wannan magana, sai ya bar ƙasar Galili, ya shiga ta Yahudiya, wadda take ƙetaren Kogin Urdun.

2. Taro mai yawan gaske suka bi shi, ya kuwa warkar da su a can.

3. Sai waɗansu Farisiyawa suka zo wurinsa su gwada shi, suka ce, “Halal ne mutum ya saki mata tasa a kan kowane dalili?”

4. Ya amsa ya ce, “Ashe, ba ku taɓa karantawa ba, cewa, wanda ya halicce su tun farko, dā ma ya yi su, namiji da tamata?”

Karanta cikakken babi Mat 19