Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mat 15:5-13 Littafi Mai Tsarki (HAU)

5. Amma ku kukan ce, ‘Kowa ya ce wa ubansa ko uwa tasa, “Duk abin da dā za ku samu a gare ni an ba Allah,” to, ba lalle ya girmama ubansa ba ke nan.’

6. Wato, saboda al'adunku kun bazanta Maganar Allah.

7. Ku munafukai! Daidai ne Ishaya ya yi annabci a kanku, da ya ce,

8. ‘Al'ummar nan a baka kawai suke girmama ni,Amma a zuci nesa suke da ni.

9. A banza suke bauta mini,Don ka'idodin da suke koyarwa umarnin ɗan adam ne.’ ”

10. Ya kira taro ya ce musu, “Ku saurara, ku fahimta.

11. Ba abin da yake shiga mutum ta baka ne yake ƙazanta shi ba, abin da yake fita ta baka yake ƙazanta mutum.”

12. Sai almajiran suka zo suka ce masa, “Ka san Farisiyawa sun ji haushi da suka ji maganan nan?”

13. Ya amsa ya ce, “Duk dashen da ba Ubana da yake Sama ne ya dasa ba, za a tumɓuke shi.

Karanta cikakken babi Mat 15