Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mat 15:11-20 Littafi Mai Tsarki (HAU)

11. Ba abin da yake shiga mutum ta baka ne yake ƙazanta shi ba, abin da yake fita ta baka yake ƙazanta mutum.”

12. Sai almajiran suka zo suka ce masa, “Ka san Farisiyawa sun ji haushi da suka ji maganan nan?”

13. Ya amsa ya ce, “Duk dashen da ba Ubana da yake Sama ne ya dasa ba, za a tumɓuke shi.

14. Ƙyale su kawai, makafin jagora ne. In kuwa makaho ya yi wa makaho jagora, ai, duk biyu sai su faɗa a rami.”

15. Amma Bitrus ya ce masa, “A yi mana fassarar misalin nan.”

16. Yesu ya ce, “Ku ma, ashe, har yanzu ba ku fahimta?

17. Ashe, ba ku gane ba, kome ya shiga mutum ta baka, cikinsa ya shiga, ta haka kuma zai fice?

18. Amma abin da ya fito ta baka, daga zuci yake, shi ne kuwa yake ƙazantar da mutum.

19. Don daga zuci mugayen tunani suke fitowa, kamar su kisankai, da zina, da fasikanci, da sata, da shaidar zur, da yanke.

20. Waɗannan suke ƙazantar da mutum. Amma a ci da hannu marar wanki ba ya ƙazantar da mutum.”

Karanta cikakken babi Mat 15