Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mat 15:1-9 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Waɗansu Farisiyawa da malaman Attaura suka zo wurin Yesu daga Urushalima, suka ce,

2. “Don me almajiranka suke keta al'adun shugabanni? Domin ba sa wanke hannu kafin su ci abinci.”

3. Sai ya amsa musu ya ce, “Ku kuma don me kuke keta umarnin Allah saboda al'adunku?

4. Domin Allah ya yi umarni ya ce, ‘Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka,’ kuma ‘Wanda ya zagi ubansa ko uwa tasa lalle a kashe shi.’

5. Amma ku kukan ce, ‘Kowa ya ce wa ubansa ko uwa tasa, “Duk abin da dā za ku samu a gare ni an ba Allah,” to, ba lalle ya girmama ubansa ba ke nan.’

6. Wato, saboda al'adunku kun bazanta Maganar Allah.

7. Ku munafukai! Daidai ne Ishaya ya yi annabci a kanku, da ya ce,

8. ‘Al'ummar nan a baka kawai suke girmama ni,Amma a zuci nesa suke da ni.

9. A banza suke bauta mini,Don ka'idodin da suke koyarwa umarnin ɗan adam ne.’ ”

Karanta cikakken babi Mat 15