24. Sa'an nan kuwa jirgin yana tsakiyar teku, raƙuman ruwa mangara tasa, gama iska tana gāba da su.
25. Wajen ƙarfe uku na dare sai Yesu ya nufo su, yana tafe a kan ruwan tekun.
26. Sa'ad da kuwa almajiran suka gan shi yana tafiya a kan ruwan, sai suka firgita suka ce, “Fatalwa ce!” Suka yi kururuwa don tsoro.