Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mat 12:8-14 Littafi Mai Tsarki (HAU)

8. Domin Ɗan Mutum shi ne Ubangijin Asabar.”

9. Sai ya ci gaba daga nan ya shiga majami'arsu.

10. Akwai wani mutum a nan kuwa mai shanyayyen hannu. Sai suka tambayi Yesu, suka ce, “Ya halatta a warkar a ran Asabar?” Wannan kuwa don su samu su kai ƙararsa ne.

11. Ya ce musu, “Misali, wane ne a cikinku in yana da tunkiya, ta faɗa a rami ran Asabar, ba zai kama ta ya fitar da ita ba?

12. Sau nawa mutum ya fi tunkiya daraja? Domin haka ya halatta a yi alheri a ran Asabar.”

13. Sa'an nan ya ce wa mutumin, “Miƙo hannunka.” Ya miƙa. Sai ya koma lafiyayye kamar ɗayan.

14. Amma Farisiyawa suka fita, suka yi shawara a kansa, yadda za su hallaka shi.

Karanta cikakken babi Mat 12