Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mat 11:4-13 Littafi Mai Tsarki (HAU)

4. Yesu ya amsa musu ya ce, “Ku je ku gaya wa Yahaya abin da kuka ji, da abin da kuka gani.

5. Makafi suna samun gani, guragu suna tafiya, ana tsarkake kutare, kurame suna ji, ana ta da matattu, ana kuma yi wa matalauta bishara.

6. Albarka tā tabbata ga wanda ba ya tuntuɓe sabili da ni.”

7. Sun tafi ke nan, sai Yesu ya fara yi wa taro maganar Yahaya, ya ce, “Kallon me kuka je yi a jeji? Kyauron da iska take kaɗawa?

8. To, kallon me kuka fita? Wani mai adon alharini? Ai kuwa, masu adon alharini a fada suke.

9. To, don me kuka fita? Ku ga wani annabi? I, lalle kuwa, har ya fi annabi nesa.

10. Wannan shi ne wanda labarinsa yake rubuce cewa,‘Ga shi, na aiko manzona ya riga ka gaba,Wanda zai shirya maka hanya gabanninka.’

11. Hakika ina gaya muku, a cikin duk waɗanda mata suka haifa, ba wanda ya bayyana da ya fi Yahaya Maibaftisma girma. Duk da haka, wanda ya fi ƙanƙanta a Mulkin Sama ya fi shi.

12. Tun daga zamanin Yahaya Maibaftisma har ya zuwa yanzu, Mulkin Sama yana shan kutse, masu kutsawa kuwa sukan riske shi.

13. Domin dukan annabawa da Attaura sun yi annabci har ya zuwa kan Yahaya.

Karanta cikakken babi Mat 11