Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mat 1:21-25 Littafi Mai Tsarki (HAU)

21. Za ta haifi ɗa, za ka kuma sa masa suna Yesu, domin shi ne zai ceci mutanensa daga zunubansu.”

22. An yi wannan ne duk, don a cika abin da Ubangiji ya faɗa ta bakin annabin cewa,

23. “Ga shi, budurwa za ta yi juna biyu, ta haifi ɗa,Za a kuma sa masa suna Immanuwel.”(Ma'anar Immanuwel kuwa itace Allah na tare da mu.)

24. Da Yusufu ya farka daga barci, sai ya bi umarnin mala'ikan Ubangiji, ya ɗauki matarsa,

25. amma bai san ta ba, sai bayan da ta haifi ɗanta, ya kuma sa masa suna Yesu.

Karanta cikakken babi Mat 1