Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mar 9:32-35 Littafi Mai Tsarki (HAU)

32. Amma fa ba su fahimci maganar ba, suna kuma jin tsoron tambaya tasa.

33. Suka zo Kafarnahum. Da ya shiga gida sai ya tambaye su, “Muhawarar me kuka yi a hanya?”

34. Amma suka yi shiru, don a hanya sun yi muhawarar ko wane ne babbansu.

35. Sai ya zauna, ya kira sha biyun nan, ya ce musu, “Kowa yake son yă zama shugaba, lalle ne yă zama na ƙarshe duka, baran kowa kuma.”

Karanta cikakken babi Mar 9