Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mar 8:8-17 Littafi Mai Tsarki (HAU)

8. Suka ci, suka ƙoshi, har suka ɗauki ragowar gutsattsarin, cike da manyan kwanduna bakwai.

9. Mutanen kuwa sun yi wajen dubu huɗu. Sai ya sallame su.

10. Nan da nan kuwa ya shiga jirgi da almajiransa, ya tafi ƙasar Dalmanuta.

11. Farisiyawa suka zo suka fara muhawara da shi, suna nema ya nuna musu wata alama daga sama, don su gwada shi.

12. Sai ya yi wata doguwar ajiyar zuciya, ya ce, “Don me mutanen zamanin nan suke neman ganin alama? Hakika, ina gaya muku, ba wata alamar da za a nuna wa mutanen wannan zamani.”

13. Daga nan ya bar su, ya sāke shiga jirgi, ya haye wancan ƙetaren.

14. Sun kuwa manta, ba su kawo gurasa ba, sai guda ɗaya ce kawai gare su a jirgin.

15. Ya gargaɗe su ya ce, “Ku kula, ku yi hankali da yistin Farisiyawa da na Hirudus.”

16. Suka yi magana da juna a kan ba su da gurasa.

17. Da yake Yesu ya gane haka, sai ya ce musu, “Don me kuke zancen ba ku da gurasa? Ashe, har yanzu ba ku gane ba, ba ku kuma fahimta ba? Zuciyarku a taurare take?

Karanta cikakken babi Mar 8