Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mar 8:6-23 Littafi Mai Tsarki (HAU)

6. Sai ya umarci taron su zauna a ƙasa. Da ya ɗauki gurasan nan bakwai, ya yi godiya ga Allah, ya gutsuttsura, ya yi ta ba almajiransa su kai wa taron, suka kuwa kakkai musu.

7. Suna kuma da ƙananan kifaye kaɗan. Da ya yi wa Allah godiya, sai ya ce su ma a kai musu.

8. Suka ci, suka ƙoshi, har suka ɗauki ragowar gutsattsarin, cike da manyan kwanduna bakwai.

9. Mutanen kuwa sun yi wajen dubu huɗu. Sai ya sallame su.

10. Nan da nan kuwa ya shiga jirgi da almajiransa, ya tafi ƙasar Dalmanuta.

11. Farisiyawa suka zo suka fara muhawara da shi, suna nema ya nuna musu wata alama daga sama, don su gwada shi.

12. Sai ya yi wata doguwar ajiyar zuciya, ya ce, “Don me mutanen zamanin nan suke neman ganin alama? Hakika, ina gaya muku, ba wata alamar da za a nuna wa mutanen wannan zamani.”

13. Daga nan ya bar su, ya sāke shiga jirgi, ya haye wancan ƙetaren.

14. Sun kuwa manta, ba su kawo gurasa ba, sai guda ɗaya ce kawai gare su a jirgin.

15. Ya gargaɗe su ya ce, “Ku kula, ku yi hankali da yistin Farisiyawa da na Hirudus.”

16. Suka yi magana da juna a kan ba su da gurasa.

17. Da yake Yesu ya gane haka, sai ya ce musu, “Don me kuke zancen ba ku da gurasa? Ashe, har yanzu ba ku gane ba, ba ku kuma fahimta ba? Zuciyarku a taurare take?

18. Kuna da idanu, ba kwa gani ne? Kuna da kunnuwa, ba kwa ji ne? Ba kwa kuma tunawa ne?

19. Da na gutsuttsura wa mutum dubu biyar gurasan nan biyar, kwando nawa kuka ɗauka cike da gutsattsarin?” Suka ce masa, “Sha biyu.”

20. “To, gurasa bakwai da na gutsuttsura wa mutum dubu huɗu fa? Manyan kwanduna nawa kuka ɗauka cike da gutsattsarin?” Suka ce masa, “Bakwai.”

21. Sai ya ce musu, “To, har yanzu ba ku fahimta ba?”

22. Suka iso Betsaida. Aka kawo masa wani makaho, aka roƙe shi ya taɓa shi.

23. Ya kama hannun makahon, ya kai shi bayan gari. Da ya tofa yau a idanunsa, ya ɗora masa hannu, sai ya tambaye shi cewa, “Kana iya ganin wani abu?”

Karanta cikakken babi Mar 8